Tuesday, 28 June 2016
KOTU TA BADA UMARNIN GARKAME KAYODE
Kotu Ta Bada Umarnin Garkame Fani
Kayode, Nenadi Usman
Wata kotun tarayya ta bada umarnin
garkame tsohon Ministan Sufurin
jiragen sama, Fani Kayode da
takwararsa na ma'aikatar kudi, Nenadi
Usman bisa zargin almundahanar
Naira Bilyan 1,5.
Mai Shari'a kotun, Suleman Hassan
ya ki bada belinsu ne bayan da
lauyan EFCC ya nemi a bashi lokaci
don yin nazari kan bukatar wadanda
ake tuhumar na neman beli.
Kudaden dai na daga cikin kudaden
makamai wadanda aka yi amfani da
su a lokacin yakin zaben Jonathan
wanda Fani Kayode ne mai Magana
da yawun kungiyar yakin neman
zaben.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment