Tuesday, 28 June 2016

KOTU TA BADA UMARNIN GARKAME KAYODE

Kotu Ta Bada Umarnin Garkame Fani Kayode, Nenadi Usman Wata kotun tarayya ta bada umarnin garkame tsohon Ministan Sufurin jiragen sama, Fani Kayode da takwararsa na ma'aikatar kudi, Nenadi Usman bisa zargin almundahanar Naira Bilyan 1,5. Mai Shari'a kotun, Suleman Hassan ya ki bada belinsu ne bayan da lauyan EFCC ya nemi a bashi lokaci don yin nazari kan bukatar wadanda ake tuhumar na neman beli. Kudaden dai na daga cikin kudaden makamai wadanda aka yi amfani da su a lokacin yakin zaben Jonathan wanda Fani Kayode ne mai Magana da yawun kungiyar yakin neman zaben.

No comments:

Post a Comment