Wednesday, 29 June 2016

AN SHAFE SAMA DA WATA UKU BABU WUTAR LANTAR KI A BORNO

AN SHAFE WATA UKU BABU HASKEN WUTAR LANTARKI A BORNO. Daga wakilin mu BIN ISMAIL ALI MAIDUGURI. Yau kimanin wata uku kenan babu hasken wutar lantarki a jihar borno, wanda haka yasa jama'a cikin kakani kayi inda, wanda har takai mai martaba shehun BORNO kira akan ayi gaggawa a samarwa jahar wutar lantarki, dan su samu susha ruwa mai sanyi a wannan wata mai albarka, amma gashi mun doshi karewan wannan wata na Ramadan amma har yanzu babu alamar wuta a jihar wanda har takai wasu na cewa, "kodai mun sallamo wutar ne baki daya. Wakilin mu ya zaka dan ganewa idanun sa yanda mutane suke rayuwa tun bayan daukewar wutar lantarki, jama'a dewa sun bayyana cewa, "abun yazo musu ne ba zata inda da wasa -wasa har yanzu mun shafe wata uku. Shi kuma assale MUHAMMAD Tahir cewa yayi, "muna cikin matsanan cin wahala na samun ruwan sha musamman a wannan wata mai albarka, inda ya kara da cewa, "in kaga wuta to sai wanda yake da hali wato yana da injin bada wutar. Sai dai duk kokarin da wakilin mu yayi na jin ta bakin jami'an wutar lantarki ya ci tura inda ya ziyarci ofishin su bai samu kowa ba.

TARIHIN T.Y BURATAI.

TARIHIN TUKUR YUSUF BURUTAI. . Lieutenant General Yusif Tukur Buratai: . Sunansa Tukur Yusuf Buratai, amma ana kiransa da ‘T.Y Buratai’. An haife shi a garin Buratai dake karamar hukumar Biu ta jihar Borno, a ranar 24 ga watan Nuwamba a shekarar 1960. Don haka, Buratai ɗan asalin jihar Borno ne dake arewa maso gabashin Najeriya. ↓ Laftana Janar TY Buratai shi ne hafsan Sojoji na 26 a tarayyar Najeriya, wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya naɗa a ranar 13 ga watan Juni na shekarar 2015. ↓ Buratai ya yi karatun Furamari a garinsu buratai, daga nan ya zarce zuwa Kwalejin Malaman Gwamnati dake garin Potiskum a jihar Yobe. A watan Junairu na shekarar 1981, Buratai ya halarci Nigerian Defence Academy dake Kaduna a matsayin ɗaya daga cikin membobi a shirin nan na ‘29 Regular Combatant Course (29R)’. Haka zalika, Buratai ya samu takardar shaidar kammala Jami’a, wato Digiri a fannin History daga Jami’ar Maiduguri. Kuma yana da Digiri a fannin Philosophy daga Jami’ar Bangladesh University of Professions dake garin Dhaka. ↓ Kafin naɗinsa a matsayin hafsan Soji, Buratai shi ke jagorantar rundunar tsaro ta hadin–gwiwa wacce ke da hedikwata a birnin Ndjamena na kasar Chadi. Kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da kuma Benin ne suka kafa rundunar domin yaki da ’yan ta’addan da ke yankinsu. ↓ A baya dai, Janar Buratai ya yi aiki a matsayin Kwamandan runduna ta Biyu ta sojin Najeriya dake birnin Fatakwal na jihar Rivers, sannan ya taba zama Kwamandan makarantar horas da sojin kasa dake Jaji, a jihar Kaduna. ↓ TY Buratai ya samu ci gaba ainun wajen aikinsa da kuma karin girma kamar haka: • Lieutenant (January 1985) • Captain (January 1989) • Major (January 1994) • Lieutenant Colonel (January 1998) • Colonel (January 2004) • Brigadier General (January 2009) • Major General (January 2012) • Lieutenant General (August 2015) ↓ TY Buratai ya samu kambi da lambobin yabo a wurare daban–daban da suka haɗa da: • Forces Service Star (FSS) • Meritorious Service Star (MSS) • Distinguished Service Star (DSS) • Grand Service Star (GSS). • Pass Staff Course Dagger (PSCD) • Field Command Medal • Training Support Medal • United Nations Medal for Angolan Verification Medal II 26-12-2015 Allah ya karawa rayuwar ka albarka T.Y burutai, ya baka ikon yin daidai, ya kare ka daga dukkan sharri, ya kuma hadaka da dukkan alkhairi. Amin.

Tuesday, 28 June 2016

KOTU TA BADA UMARNIN GARKAME KAYODE

Kotu Ta Bada Umarnin Garkame Fani Kayode, Nenadi Usman Wata kotun tarayya ta bada umarnin garkame tsohon Ministan Sufurin jiragen sama, Fani Kayode da takwararsa na ma'aikatar kudi, Nenadi Usman bisa zargin almundahanar Naira Bilyan 1,5. Mai Shari'a kotun, Suleman Hassan ya ki bada belinsu ne bayan da lauyan EFCC ya nemi a bashi lokaci don yin nazari kan bukatar wadanda ake tuhumar na neman beli. Kudaden dai na daga cikin kudaden makamai wadanda aka yi amfani da su a lokacin yakin zaben Jonathan wanda Fani Kayode ne mai Magana da yawun kungiyar yakin neman zaben.

Sunday, 12 June 2016

JIHAR BORNO TA SHAFE SAMA DA WATA DAYA BABU WUTAR LANTAR KI.

Al-ummar jihar borno sun shafe sama da wata daya, basu da wutar lantar ki, kuma suna cikin matsanan cin wahala saboda yanayin zafin da suke ciki kuma basa samun ruwan sha mai sanyi, yanda ya kamata, kwamakin baya mai martaba shehun borno Umar Garbai el-amin elkanami, yayi kira da a gaggauta kawo wuta dan al'umma ta samu sa'idar rayuwa, amma har yanzu suna fiskan tar wannan matsala, inda zafin rana yana kai wa digiri 40% na rana, wanda yasa al'umma dewa na jikkata. Da muka tun tubi wani babban jami'in wutar lantar ki na jaha wanda bai son bayyana sunan sa ba, yace, "Wasu manyan tirasfomomi ne suka lalace akan hanyar Biu zuwa maiduguri, kuma yace, "injinonin su suna kan gyarawa dan haka al'umma suci gaba da hakuri.

Sunday, 28 February 2016

SHIGA NAN DAN KA BADA SHAWARA.


MUNA BUKATAR KU BAIYA NA MANA RA'AYIN KU DAN GANE DA YANDA MUKE WATSO MUKU SHIRYE SHIRYEN MU, ZAKU IYA BAIYANA A NAN KASA DON MU SAMU KARFIN GWIWAR AIKA MUNA GODIYA BAIYA NA RA'AYIN KA YANZU.

Modu Sheriff Ne Yake Daukar Nauyin Boko Haram - Inji Kayode

Rikici tsakanin Sabon Shugaban Jam’iyar PDPda tsohon Ministan tsohon shugaban kasa Jonathan, Fani Kayode ya barke inda suka sa juna a gaba domin tona asirin juna.A inda Kayode ya kira Ali Modu Sheriff “Mai daukar nauyin Boko Haram” Ali Modu Sheriff ya maida martani yace masa “da abinda kake fada gaskiyane da Buhari ya kamani tuntuni”.A halin da ake ciki yanzu dai Ali Modu sheriff ya shigar da kara Kotu ta dalilin zargin da Kayode yake masa akan ya biya shi naira Biliyan 10 sannan kuma ya bukaci ya fito duniya ya bashi hakuri, sannan ya tabbatarwa da duniya cewar, "sai yayi maganin Fani Kayode".Mudai fatan mu shine Allah ya kara tona asirinazzalumai a kasar nan.

Saturday, 27 February 2016

BUHARI NA SHIRIN MAYAR DA KASAR NAN TA ISLAMA-FAYOSE

Buhari Na Shirye-shiryen Mayar Da Nijeriya Kasar Islama, Inji Gwamna Fayose *Ya Kuma Ce PDP Za Ta Dawo A 2019 Daga Sani Musa, Abuja Gwanan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ya yi zargin cewa shugaba Muhammadu Buhari yana kule-kulen mayar da Nijeriya kasar islama. Ayodele Fayose ya yi wannan zargin ne a garin Fatakwal babban birnin jihar Ribas, wajen bikin adu'ar godewa Allah dangane da nasara da takwaran sa na jihar Ribas Nyesom Wike ya yi a kotun koli. Gwamnan wanda ya bayyana kansa a matsayin mai ki fadi wanda ya ce babu wanda ya isa ya taba shi, ya shedawa jama'ar da suka halarci taron adu'ar cewa yana wani sirri da zai bayyana masu, inda ya yi tambayr su ko suna son jin wannan sirrin dangane da Shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma gwanatinsa da APC? Sai Gwamna Fayose yace "suna nan suna shirye-shirye mayar da kasar nan mai bin tafarkin addinin Islama kuma hakar su ba za ta cimma ruwa ba, kamar yadda ba su samu nasarar yin hakan ba a shekara ta 1984." Gwamnan ya ce idan babu lauje cikin ladi, menene ya sa mutum biyar suka tafi kasar Saudiya suka jira shugaban kasar a can idan ba su da wata manufa? Ya ce sannu a hankali Allah na tona asirin su, ya ce Nijeriya kasa ce mai tsarin addinai barkatai kuma babu wanda ya isa ya hana wani yin Kiristanci kuma Musulmai su yi nasu. Gwamnan ya ce babu ko tantama PDP za ta dawo mulkin kasar nan a shekara ta 2019.