Saturday, 27 February 2016
BUHARI NA SHIRIN MAYAR DA KASAR NAN TA ISLAMA-FAYOSE
Buhari Na Shirye-shiryen Mayar Da
Nijeriya Kasar Islama, Inji Gwamna
Fayose
*Ya Kuma Ce PDP Za Ta Dawo A
2019
Daga Sani Musa, Abuja
Gwanan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ya
yi zargin cewa shugaba Muhammadu
Buhari yana kule-kulen mayar da
Nijeriya kasar islama.
Ayodele Fayose ya yi wannan zargin
ne a garin Fatakwal babban birnin
jihar Ribas, wajen bikin adu'ar
godewa Allah dangane da nasara da
takwaran sa na jihar Ribas Nyesom
Wike ya yi a kotun koli.
Gwamnan wanda ya bayyana kansa a
matsayin mai ki fadi wanda ya ce
babu wanda ya isa ya taba shi, ya
shedawa jama'ar da suka halarci
taron adu'ar cewa yana wani sirri da
zai bayyana masu, inda ya yi tambayr
su ko suna son jin wannan sirrin
dangane da Shugaban kasa
Muhammadu Buhari da kuma
gwanatinsa da APC?
Sai Gwamna Fayose yace "suna nan
suna shirye-shirye mayar da kasar
nan mai bin tafarkin addinin Islama
kuma hakar su ba za ta cimma ruwa
ba, kamar yadda ba su samu nasarar
yin hakan ba a shekara ta 1984."
Gwamnan ya ce idan babu lauje cikin
ladi, menene ya sa mutum biyar suka
tafi kasar Saudiya suka jira shugaban
kasar a can idan ba su da wata
manufa?
Ya ce sannu a hankali Allah na tona
asirin su, ya ce Nijeriya kasa ce mai
tsarin addinai barkatai kuma babu
wanda ya isa ya hana wani yin
Kiristanci kuma Musulmai su yi nasu.
Gwamnan ya ce babu ko tantama
PDP za ta dawo mulkin kasar nan a
shekara ta 2019.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment