Saturday, 27 February 2016
BANYI WA KOWA ALKAWARIN DUBU BIYAR BA-BUHARI
Ban yiwa kowa alkawalin naira dubu
biyar ba, inji Buhari a Saudiyya.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari
ya
tabbatar da cewar ba inda yace zai
baiwa matasa kyauta naira dubu biyar
duk wata a lokacin kamfen dinsa.
A jawabin da ya yiwa yan Najeriya
Mazauna Saudiyya yace zancen
baiwa
matasa marasa aiki na naira dubu
biyar
zance ne a cikin manufofin kamfe na
jam'iyyar APC ba na Muhammadu
Buhari a matsayin dan takara ba.
Haka ma ya roki yan Najeriya dake
kasar Saudiyya dasu taimakawa
kasarsu da addu'oi don kuwa
matsalolin
da kasar take fuskanta ba zai iya
kawo
kashe ba, sai da addua.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment