Saturday, 27 February 2016
WATA DODONNIYA TA BULLA A GASHIWA TANA SHA JINI
Hatsabibiyar Dodanniya Ta Bulla Da
Shan Jini A Gashua
— Muhammad Maitela
Wasu bayanai da LEADERSHIP Hausa
ta samu daga jama’a da dama a
Unguwanni daban-daban da ke garin
Gashuwa ta jihar Yobe, sun nuna
cewa jama’a suna ci gaba da fargaba
dangane da yadda wata halitta mai
kama da Dodanniya ke shiga gidajen
jama’a tana yin awon gaba da
dabbobinsu, wanda daga bisani sai a
tarar an kwashe kayan cikin dabbar
an bar gangar jikin, a wani lokaci
kuma sai a tarar da dabbar kwance
an tsotse jininta.
Bayanan suka nuna cewa, wannan
babban abin al’ajabi yana ci gaba da
daure wa jama’a da dama kai, bisa
yadda matsalar ke ci gaba da yi masu
barazanar da ta kai wasu ba sa
samun runtsawa, yayin da wasu ke
sintiri don tsaron unguwannin nasu
har gari ya waye.
Wani mazaunin wannan wuri, Malam
Muhammed Abbas (Malam Awan) ya
bayyana cewa, “hakika wannan
al’amarin ya daure mana kai. Saboda
ranar Jumu’ar da ta gabata, wannan
Dodanniyar ta shiga gidan
makwabcina ta kama tunkiya, inda ta
kwashe kayan cikinta, ta bar gangar
jikin a kofar gida. Kashe gari kuma ya
sake dawowa, to shi ne sai muka
fahimci abin ba na zama ba ne, sai
muka fara tunanin kada fa wannan
abin ya tsallaka zuwa ga ‘ya’yanmu.”
Ya ci gaba da cewa, “hakan ta sa
muka yi shawarar cewa ba mu ga ta
zama ba,inda muka nemi matasan
Unguwa majiya karfi muka rarraba su
kashi-kashi a cikin Unguwar, wasu a
kan itace, kuma kowanne rike da
sanduna da fitilar hannu; can cikin
salasainin dare sai muka gansu sun
tunkaro mu su biyu, shi ne daya daga
cikinmu ya dalla masu hasken fitila,
cikin tsoro sai suka fita a guje, muka
bi su,mutane sun tasamma dari, daya
daga cikin Dodannin, wajen shan
kwana sai da ya yi karo da katanga,
kamar ya fadi, a haka ya shanye
kwanar. Kuma abin mamaki, hatta
karnuka da suka gansu, fadawa cikin
gida suka yi, kuma kafafunsu hudu
ne kamar dangin kura, kuma kamar
mutum daga gaba, sannan babu jela,
amma da muka rutsa shi sai ya bata
bat.”
Malamin ya kara da bayyana
cewa,suna cikin matukar fargabar
wannan al’amarin, inda ya ce,
“kasancewar yadda wannan abu ke
mana ta’adi, musamman yadda ba ya
kama ramammen rago ko tinkiya, sai
kosasshe, kuma ba ya cin akuya,
yanzu haka wasu sun sayar da
dabbobin su. Sannan yanzu mun yi
shawarar mu hadu mu gaya wa
Sarkin Bade halin da ake ciki.
Sannan za mu shaida wa jami’an
tsaron ’yan sanda da sojoji don
gudun kada matsalar ta wuce inda
take yanzu. Amma gaskiya muna
fuskantar damuwa.”
Ita kuma Malama Jimmala, wacce
wannan abu ya sungume mata
tinkiya, sannan ya wawushe kayan
cikinta ya jefar da ita a kofar gida, ta
bayyana cewa, “da misalin karfe biyu
muna daki sai muka ji motsi a waje,
dayake mun dan tsorata, ba mu fito
ba, shiru har gari ya waye, shi ne sai
muka ga babu tinkiyarmu, mun dauka
ko barawo ne, abin mamaki sai muka
ganta a kofar gida a mace bayan an
kwashe kayan cikinta. Sannan wani
abin mamaki, babu wata alamar jini
ya zuba.”
Bisa ga bayanan da wakilinmu ya
tattaro a garin, sun bayyana cewa
wannan Dodo ya karade Unguwanni
da dama, tare da hallaka dabbobi
masu yawa, sannan kuma duk wani
abu da jama’a ke yi ta hanyar yi
masa a-tare, abin ya faskara. Saboda
wani lokaci sai an yi masa kofar
rago, amma sai ya sulale a rasa inda
ya shiga.
Amma dai wasu da suka sha yin
arangama da ita sun ce, wani lokaci
ta kan zo a siffar mutum, wani zubin
kuma kamar kura, amma babu jela.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment