Saturday, 27 February 2016
El'rufa'i yayi kuskure akan dokan wa'azi-inji majalisar malamai
El Rufa'i Ya Tafka Kuskure Akan
Dokokin Wa'azi Da Ya Kafa, Inji
Majalisar Limamai Da Malamai Ta
Jihar Kaduna
DAGA IBRAHIM AMMANI, KADUNA
Majalisar Limamai da Malaman Jihar
Kaduna, ta yi tir gami da Allah wadai,
akan matakin da gwamnan jihar,
Malam Nasiru El-Rufa'i ya dauka, na
kaddamar da dokokin wa'azi a jihar.
Da yake bayani gaban manema
labarai a Kaduna, Shugaban Majalisar
Malaman, Al Sheik Usman Baban
Tune, ya ce da akwai kuskure babba
da gwamnan ya yi na yin kokarin
shiga sabga ta Addini, da yin
katsalandan akan harkar ta Malamta,
wanda wannan inji Malamin ba
karamar tawayace zai haifar a cikin
tsarin gwamnatinsa ba.
Shugaban Majalisar Malaman ya ci
gaba da cewar, sun shiga cikin wani
yanayi lokacin da suka ga takardar
dokokin Wa'azin wacce aka rubutata
cikin harshen Turanci, kuma nan take
suka sa aka fassara ta zuwa harshen
Hausa, sannan aka rarraba ta ga
Malamai da Limamai dake Jihar
domin kara fahimtar Takardar, sannan
suka yi shiri na musanman zuwa
Majalisar Dokokin jihar inda suka
gana da Shugaban Majalisar dokokin
da sauran Wakilan Majalisar akan
lamarin, kuma bisa ga dukkan alamu
'Yan Majalisun dokokin suna da
fahimta da tarbiyar addini, domin sun
tabbatar musu ba za su amince da
wannan doka ba har sai idan sun yi
zama da Malamai.
Sheik Baban Tune, ya kara da cewar,
gwamnati ta Musulunci dake
taimakawa Musulunci, ita ce take da
damar tsarawa Malamai yadda za su
gudanar da Wa'azi, ba Gwamnatin da
ta yi hannun riga da Musulunci ba,
babu wani tagomashin da Musulunci
ko Malaman Musulunci suke samu
daga gareta.
Malamin ya bayyana cewa, dukkanin
Malaman Musulunci da na Kiristanci
a Jihar, sun yi tarayya wajen la'antar
wannan kuduri na gwamnan, domin
babu alama na fahimta a ciki, saboda
a cikin takardar dokokin an bayyana
cewar, za a kafa wata hukuma wacce
JNI da CAN za su kasance a
karkashinta, sannan wannan hukuma
za ta sanya ido akan harkar wa'azi,
karkashin mai baiwa gwamna
shawara akan harkar tsaro, da
wakilcin 'yan sanda, da bangaren
Shari'a, inda ya ce wannan kadai ya
isa ya nuna rashin adalci.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment