Wednesday, 29 June 2016
AN SHAFE SAMA DA WATA UKU BABU WUTAR LANTAR KI A BORNO
AN SHAFE WATA UKU BABU HASKEN WUTAR LANTARKI A BORNO.
Daga wakilin mu BIN ISMAIL ALI MAIDUGURI.
Yau kimanin wata uku kenan babu hasken wutar lantarki a jihar borno, wanda haka yasa jama'a cikin kakani kayi inda, wanda har takai mai martaba shehun BORNO kira akan ayi gaggawa a samarwa jahar wutar lantarki, dan su samu susha ruwa mai sanyi a wannan wata mai albarka, amma gashi mun doshi karewan wannan wata na Ramadan amma har yanzu babu alamar wuta a jihar wanda har takai wasu na cewa, "kodai mun sallamo wutar ne baki daya.
Wakilin mu ya zaka dan ganewa idanun sa yanda mutane suke rayuwa tun bayan daukewar wutar lantarki, jama'a dewa sun bayyana cewa, "abun yazo musu ne ba zata inda da wasa -wasa har yanzu mun shafe wata uku. Shi kuma assale MUHAMMAD Tahir cewa yayi, "muna cikin matsanan cin wahala na samun ruwan sha musamman a wannan wata mai albarka, inda ya kara da cewa, "in kaga wuta to sai wanda yake da hali wato yana da injin bada wutar.
Sai dai duk kokarin da wakilin mu yayi na jin ta bakin jami'an wutar lantarki ya ci tura inda ya ziyarci ofishin su bai samu kowa ba.
TARIHIN T.Y BURATAI.
TARIHIN TUKUR YUSUF
BURUTAI.
.
Lieutenant General Yusif Tukur
Buratai:
.
Sunansa Tukur Yusuf Buratai, amma
ana kiransa da ‘T.Y Buratai’. An haife
shi a garin Buratai dake karamar
hukumar Biu ta jihar Borno, a ranar
24 ga watan Nuwamba a shekarar
1960. Don haka,
Buratai ɗan asalin jihar Borno ne
dake arewa
maso gabashin Najeriya.
↓
Laftana Janar TY Buratai shi ne
hafsan Sojoji na
26 a tarayyar Najeriya, wanda
shugaban kasa
Muhammadu Buhari ya naɗa a ranar
13 ga watan
Juni na shekarar 2015.
↓
Buratai ya yi karatun Furamari a
garinsu buratai, daga nan ya zarce
zuwa Kwalejin
Malaman Gwamnati dake garin
Potiskum a jihar Yobe. A watan
Junairu na shekarar 1981, Buratai ya
halarci Nigerian Defence
Academy dake Kaduna a
matsayin ɗaya daga cikin
membobi a shirin nan
na ‘29 Regular Combatant Course
(29R)’. Haka zalika, Buratai ya samu
takardar
shaidar kammala Jami’a, wato Digiri
a fannin History daga Jami’ar
Maiduguri. Kuma yana da Digiri a
fannin Philosophy daga Jami’ar
Bangladesh
University of Professions dake garin
Dhaka.
↓
Kafin naɗinsa a matsayin hafsan Soji,
Buratai shi
ke jagorantar rundunar tsaro ta
hadin–gwiwa
wacce ke da hedikwata a birnin
Ndjamena na kasar Chadi. Kasashen
Najeriya
da Nijar da Kamaru da Chadi da kuma
Benin ne suka kafa rundunar domin
yaki da ’yan ta’addan da ke yankinsu.
↓
A baya dai, Janar Buratai ya yi aiki a
matsayin
Kwamandan runduna ta Biyu ta sojin
Najeriya
dake birnin Fatakwal na jihar Rivers,
sannan ya
taba zama Kwamandan
makarantar horas da
sojin kasa dake Jaji, a jihar
Kaduna.
↓
TY Buratai ya samu ci gaba ainun
wajen aikinsa
da kuma karin girma kamar haka:
• Lieutenant (January 1985)
• Captain (January 1989)
• Major (January 1994)
• Lieutenant Colonel (January 1998)
• Colonel (January 2004)
• Brigadier General (January 2009)
• Major General (January 2012)
• Lieutenant General (August 2015)
↓
TY Buratai ya samu kambi da
lambobin yabo a
wurare daban–daban da suka haɗa
da:
• Forces Service Star (FSS)
• Meritorious Service Star (MSS)
• Distinguished Service Star (DSS)
• Grand Service Star (GSS).
• Pass Staff Course Dagger (PSCD)
• Field Command Medal
• Training Support Medal
• United Nations Medal for Angolan
Verification
Medal II 26-12-2015
Allah ya karawa rayuwar ka albarka
T.Y burutai,
ya baka ikon yin daidai, ya kare ka
daga dukkan
sharri, ya kuma hadaka da dukkan
alkhairi. Amin.
Tuesday, 28 June 2016
KOTU TA BADA UMARNIN GARKAME KAYODE
Kotu Ta Bada Umarnin Garkame Fani
Kayode, Nenadi Usman
Wata kotun tarayya ta bada umarnin
garkame tsohon Ministan Sufurin
jiragen sama, Fani Kayode da
takwararsa na ma'aikatar kudi, Nenadi
Usman bisa zargin almundahanar
Naira Bilyan 1,5.
Mai Shari'a kotun, Suleman Hassan
ya ki bada belinsu ne bayan da
lauyan EFCC ya nemi a bashi lokaci
don yin nazari kan bukatar wadanda
ake tuhumar na neman beli.
Kudaden dai na daga cikin kudaden
makamai wadanda aka yi amfani da
su a lokacin yakin zaben Jonathan
wanda Fani Kayode ne mai Magana
da yawun kungiyar yakin neman
zaben.
Sunday, 12 June 2016
JIHAR BORNO TA SHAFE SAMA DA WATA DAYA BABU WUTAR LANTAR KI.
Al-ummar jihar borno sun shafe sama da wata daya, basu da wutar lantar ki, kuma suna cikin matsanan cin wahala saboda yanayin zafin da suke ciki kuma basa samun ruwan sha mai sanyi, yanda ya kamata, kwamakin baya mai martaba shehun borno Umar Garbai el-amin elkanami, yayi kira da a gaggauta kawo wuta dan al'umma ta samu sa'idar rayuwa, amma har yanzu suna fiskan tar wannan matsala, inda zafin rana yana kai wa digiri 40% na rana, wanda yasa al'umma dewa na jikkata.
Da muka tun tubi wani babban jami'in wutar lantar ki na jaha wanda bai son bayyana sunan sa ba, yace, "Wasu manyan tirasfomomi ne suka lalace akan hanyar Biu zuwa maiduguri, kuma yace, "injinonin su suna kan gyarawa dan haka al'umma suci gaba da hakuri.
Sunday, 28 February 2016
SHIGA NAN DAN KA BADA SHAWARA.
Modu Sheriff Ne Yake Daukar Nauyin Boko Haram - Inji Kayode
Rikici tsakanin Sabon Shugaban Jam’iyar PDPda tsohon Ministan tsohon shugaban kasa Jonathan, Fani Kayode ya barke inda suka sa juna a gaba domin tona asirin juna.A inda Kayode ya kira Ali Modu Sheriff “Mai daukar nauyin Boko Haram” Ali Modu Sheriff ya maida martani yace masa “da abinda kake fada gaskiyane da Buhari ya kamani tuntuni”.A halin da ake ciki yanzu dai Ali Modu sheriff ya shigar da kara Kotu ta dalilin zargin da Kayode yake masa akan ya biya shi naira Biliyan 10 sannan kuma ya bukaci ya fito duniya ya bashi hakuri, sannan ya tabbatarwa da duniya cewar, "sai yayi maganin Fani Kayode".Mudai fatan mu shine Allah ya kara tona asirinazzalumai a kasar nan.
Saturday, 27 February 2016
BUHARI NA SHIRIN MAYAR DA KASAR NAN TA ISLAMA-FAYOSE
Buhari Na Shirye-shiryen Mayar Da
Nijeriya Kasar Islama, Inji Gwamna
Fayose
*Ya Kuma Ce PDP Za Ta Dawo A
2019
Daga Sani Musa, Abuja
Gwanan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ya
yi zargin cewa shugaba Muhammadu
Buhari yana kule-kulen mayar da
Nijeriya kasar islama.
Ayodele Fayose ya yi wannan zargin
ne a garin Fatakwal babban birnin
jihar Ribas, wajen bikin adu'ar
godewa Allah dangane da nasara da
takwaran sa na jihar Ribas Nyesom
Wike ya yi a kotun koli.
Gwamnan wanda ya bayyana kansa a
matsayin mai ki fadi wanda ya ce
babu wanda ya isa ya taba shi, ya
shedawa jama'ar da suka halarci
taron adu'ar cewa yana wani sirri da
zai bayyana masu, inda ya yi tambayr
su ko suna son jin wannan sirrin
dangane da Shugaban kasa
Muhammadu Buhari da kuma
gwanatinsa da APC?
Sai Gwamna Fayose yace "suna nan
suna shirye-shirye mayar da kasar
nan mai bin tafarkin addinin Islama
kuma hakar su ba za ta cimma ruwa
ba, kamar yadda ba su samu nasarar
yin hakan ba a shekara ta 1984."
Gwamnan ya ce idan babu lauje cikin
ladi, menene ya sa mutum biyar suka
tafi kasar Saudiya suka jira shugaban
kasar a can idan ba su da wata
manufa?
Ya ce sannu a hankali Allah na tona
asirin su, ya ce Nijeriya kasa ce mai
tsarin addinai barkatai kuma babu
wanda ya isa ya hana wani yin
Kiristanci kuma Musulmai su yi nasu.
Gwamnan ya ce babu ko tantama
PDP za ta dawo mulkin kasar nan a
shekara ta 2019.
BANYI WA KOWA ALKAWARIN DUBU BIYAR BA-BUHARI
Ban yiwa kowa alkawalin naira dubu
biyar ba, inji Buhari a Saudiyya.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari
ya
tabbatar da cewar ba inda yace zai
baiwa matasa kyauta naira dubu biyar
duk wata a lokacin kamfen dinsa.
A jawabin da ya yiwa yan Najeriya
Mazauna Saudiyya yace zancen
baiwa
matasa marasa aiki na naira dubu
biyar
zance ne a cikin manufofin kamfe na
jam'iyyar APC ba na Muhammadu
Buhari a matsayin dan takara ba.
Haka ma ya roki yan Najeriya dake
kasar Saudiyya dasu taimakawa
kasarsu da addu'oi don kuwa
matsalolin
da kasar take fuskanta ba zai iya
kawo
kashe ba, sai da addua.
LABARU DA DUMI DUMI WANI BOM YA TASHI A KAMARUN
Rahotanni daga garin BANGUR da ke
Lardin Arewa mai Nisa Sun tabbatar
da cewa Wani BOMB ya tashi a
garin. Wanda hakan yayi Sanadiyyar
mutuwar Wasu Sojoji. Har ma Ana
cewa Lamarin ya ritsa da dagacin
garin.
WATA DODONNIYA TA BULLA A GASHIWA TANA SHA JINI
Hatsabibiyar Dodanniya Ta Bulla Da
Shan Jini A Gashua
— Muhammad Maitela
Wasu bayanai da LEADERSHIP Hausa
ta samu daga jama’a da dama a
Unguwanni daban-daban da ke garin
Gashuwa ta jihar Yobe, sun nuna
cewa jama’a suna ci gaba da fargaba
dangane da yadda wata halitta mai
kama da Dodanniya ke shiga gidajen
jama’a tana yin awon gaba da
dabbobinsu, wanda daga bisani sai a
tarar an kwashe kayan cikin dabbar
an bar gangar jikin, a wani lokaci
kuma sai a tarar da dabbar kwance
an tsotse jininta.
Bayanan suka nuna cewa, wannan
babban abin al’ajabi yana ci gaba da
daure wa jama’a da dama kai, bisa
yadda matsalar ke ci gaba da yi masu
barazanar da ta kai wasu ba sa
samun runtsawa, yayin da wasu ke
sintiri don tsaron unguwannin nasu
har gari ya waye.
Wani mazaunin wannan wuri, Malam
Muhammed Abbas (Malam Awan) ya
bayyana cewa, “hakika wannan
al’amarin ya daure mana kai. Saboda
ranar Jumu’ar da ta gabata, wannan
Dodanniyar ta shiga gidan
makwabcina ta kama tunkiya, inda ta
kwashe kayan cikinta, ta bar gangar
jikin a kofar gida. Kashe gari kuma ya
sake dawowa, to shi ne sai muka
fahimci abin ba na zama ba ne, sai
muka fara tunanin kada fa wannan
abin ya tsallaka zuwa ga ‘ya’yanmu.”
Ya ci gaba da cewa, “hakan ta sa
muka yi shawarar cewa ba mu ga ta
zama ba,inda muka nemi matasan
Unguwa majiya karfi muka rarraba su
kashi-kashi a cikin Unguwar, wasu a
kan itace, kuma kowanne rike da
sanduna da fitilar hannu; can cikin
salasainin dare sai muka gansu sun
tunkaro mu su biyu, shi ne daya daga
cikinmu ya dalla masu hasken fitila,
cikin tsoro sai suka fita a guje, muka
bi su,mutane sun tasamma dari, daya
daga cikin Dodannin, wajen shan
kwana sai da ya yi karo da katanga,
kamar ya fadi, a haka ya shanye
kwanar. Kuma abin mamaki, hatta
karnuka da suka gansu, fadawa cikin
gida suka yi, kuma kafafunsu hudu
ne kamar dangin kura, kuma kamar
mutum daga gaba, sannan babu jela,
amma da muka rutsa shi sai ya bata
bat.”
Malamin ya kara da bayyana
cewa,suna cikin matukar fargabar
wannan al’amarin, inda ya ce,
“kasancewar yadda wannan abu ke
mana ta’adi, musamman yadda ba ya
kama ramammen rago ko tinkiya, sai
kosasshe, kuma ba ya cin akuya,
yanzu haka wasu sun sayar da
dabbobin su. Sannan yanzu mun yi
shawarar mu hadu mu gaya wa
Sarkin Bade halin da ake ciki.
Sannan za mu shaida wa jami’an
tsaron ’yan sanda da sojoji don
gudun kada matsalar ta wuce inda
take yanzu. Amma gaskiya muna
fuskantar damuwa.”
Ita kuma Malama Jimmala, wacce
wannan abu ya sungume mata
tinkiya, sannan ya wawushe kayan
cikinta ya jefar da ita a kofar gida, ta
bayyana cewa, “da misalin karfe biyu
muna daki sai muka ji motsi a waje,
dayake mun dan tsorata, ba mu fito
ba, shiru har gari ya waye, shi ne sai
muka ga babu tinkiyarmu, mun dauka
ko barawo ne, abin mamaki sai muka
ganta a kofar gida a mace bayan an
kwashe kayan cikinta. Sannan wani
abin mamaki, babu wata alamar jini
ya zuba.”
Bisa ga bayanan da wakilinmu ya
tattaro a garin, sun bayyana cewa
wannan Dodo ya karade Unguwanni
da dama, tare da hallaka dabbobi
masu yawa, sannan kuma duk wani
abu da jama’a ke yi ta hanyar yi
masa a-tare, abin ya faskara. Saboda
wani lokaci sai an yi masa kofar
rago, amma sai ya sulale a rasa inda
ya shiga.
Amma dai wasu da suka sha yin
arangama da ita sun ce, wani lokaci
ta kan zo a siffar mutum, wani zubin
kuma kamar kura, amma babu jela.
SARAKI YA SIRKA TSIYA, YA KASHE MILYON 300,
Saraki Ya Sayi Motocin Alfarma Na
Milyoyin Kudade Duk Da Fama Da
Matsalar Tattalin Arzikin Kasa Da Ake
Yi
Duk da matsanancin rashin kudi da
tattalin da Gwamnatin Tarayya ta ke
yi wajen tanada kudaden kasa domin
yin ayyukan ci gaban kasa, shugaban
majalisar Dattawa Sanata Bukola
Saraki ya canza motocin hawansa,
inda zuwa yanzu dai guda hudu ne
suka riga suka zo, kuma har ya fara
amfani da su. Rahotanni sun nuna
cewa an kashe sama da Naira
Miliyan 300 wajen siyansu.
Sauran guda shidan da suka rage
suna kan hanya.
Cikin motocin da suke kasa yanzu
sun hada da mota kirar Marsandi
(2016) akan Naira Miliyan 49 ko
wace daya da mota kirar Toyota
(2016) akan kudi sama da Naira
Miliyan 100.
Majiya: Premium Times
El'rufa'i yayi kuskure akan dokan wa'azi-inji majalisar malamai
El Rufa'i Ya Tafka Kuskure Akan
Dokokin Wa'azi Da Ya Kafa, Inji
Majalisar Limamai Da Malamai Ta
Jihar Kaduna
DAGA IBRAHIM AMMANI, KADUNA
Majalisar Limamai da Malaman Jihar
Kaduna, ta yi tir gami da Allah wadai,
akan matakin da gwamnan jihar,
Malam Nasiru El-Rufa'i ya dauka, na
kaddamar da dokokin wa'azi a jihar.
Da yake bayani gaban manema
labarai a Kaduna, Shugaban Majalisar
Malaman, Al Sheik Usman Baban
Tune, ya ce da akwai kuskure babba
da gwamnan ya yi na yin kokarin
shiga sabga ta Addini, da yin
katsalandan akan harkar ta Malamta,
wanda wannan inji Malamin ba
karamar tawayace zai haifar a cikin
tsarin gwamnatinsa ba.
Shugaban Majalisar Malaman ya ci
gaba da cewar, sun shiga cikin wani
yanayi lokacin da suka ga takardar
dokokin Wa'azin wacce aka rubutata
cikin harshen Turanci, kuma nan take
suka sa aka fassara ta zuwa harshen
Hausa, sannan aka rarraba ta ga
Malamai da Limamai dake Jihar
domin kara fahimtar Takardar, sannan
suka yi shiri na musanman zuwa
Majalisar Dokokin jihar inda suka
gana da Shugaban Majalisar dokokin
da sauran Wakilan Majalisar akan
lamarin, kuma bisa ga dukkan alamu
'Yan Majalisun dokokin suna da
fahimta da tarbiyar addini, domin sun
tabbatar musu ba za su amince da
wannan doka ba har sai idan sun yi
zama da Malamai.
Sheik Baban Tune, ya kara da cewar,
gwamnati ta Musulunci dake
taimakawa Musulunci, ita ce take da
damar tsarawa Malamai yadda za su
gudanar da Wa'azi, ba Gwamnatin da
ta yi hannun riga da Musulunci ba,
babu wani tagomashin da Musulunci
ko Malaman Musulunci suke samu
daga gareta.
Malamin ya bayyana cewa, dukkanin
Malaman Musulunci da na Kiristanci
a Jihar, sun yi tarayya wajen la'antar
wannan kuduri na gwamnan, domin
babu alama na fahimta a ciki, saboda
a cikin takardar dokokin an bayyana
cewar, za a kafa wata hukuma wacce
JNI da CAN za su kasance a
karkashinta, sannan wannan hukuma
za ta sanya ido akan harkar wa'azi,
karkashin mai baiwa gwamna
shawara akan harkar tsaro, da
wakilcin 'yan sanda, da bangaren
Shari'a, inda ya ce wannan kadai ya
isa ya nuna rashin adalci.
YAN BOKO-HARAM KUSAN 30, SUKA MIKA WUYA.
Rahotanni daga Damboa dake jihar borno na cewa، "Akalla yan Boko-Haram 30, ne suka mika wuya ga sojojin nigeria inda sun ce,"sun gaji da yaki ne kuma basu da yanda zasuyi shine sun mika wuya, dan gwamnatin nigeria tayi musu afwa.
Haka lamarin yake a SABONGARI dake karamar hukumar Damboa inda su kuma yan Boko-Haram guda biyu 2 ne sun mika makaman su ga sojoji.
Sai dai a gefe guda kuma al'ummar yankin suna kira ga sojoji kada su karbi afuwan yan ta'adda a cewar su a kashe su kawai.
Sai dai masu sharhi na cewa, "in da gaske ne suka sallama a karbe su sannan a samu wani guri a juye musu wannan muguwar akida sannan daga baya gwamnati ta samar musu da aikin yi, suka ce idan har an kashe su idan wasu suna da niyyar yin haka to bazasuyi ba zasu gwammace su mutu.
A NAKU TUNANIN YA GWAMNATI ZATAYI DA WADAN DA SUKA MIKA WUYA
KUNA IYA AIKO MANA DA LABARU TA EMAIL.
KUNA IYA AIKO MANA DA LABARU TA ADRESHIN MU NA EMAIL A BORNOHAUSA@GMAIL.COM SAI KUCI GABA DA AIKO MANA LABARU DA YANA YIN WAJA JEN KU. MUNGODE.
BAZAMU HANA YANCIN MAGANA BA-SARAKI
Ba Za Mu Samar Da Dokar 'Yancin
Fadin Albarkacin Baki Ba A Kafafen
Sadarwa, Inji Shugaban Majalisar
Dattijai, Sanata Bukola Sadaki
Fadin Albarkacin Baki Ba A Kafafen
Sadarwa, Inji Shugaban Majalisar
Dattijai, Sanata Bukola Sadaki
GEN.BURATAI YA BUDE HANYAR DAMBOA
A safiyar yau ne shugaban rundunar sojoji gen buratai ya bude hanyar da ta tashi daga maiduguri zuwa Damboa, gen buratai shine ya jagoran ci bude hanya, inda masu gani da ido suka ce, "Sunga al'ummar Damboa wadan da rikicin Boko Haram ya tilas ta musu fita daga cikin gari Damboa suna ta murna tare da jin jinawa shugaban sojojin buratai.
Haka lamarin yake a can karamar hukumar Damboa jama'a da dama ne suka fito akan titi dan tarbar ayarin sojoji da kuma wasu jama'a da suka bi tawagar.
Haka lamarin yake a can karamar hukumar Damboa jama'a da dama ne suka fito akan titi dan tarbar ayarin sojoji da kuma wasu jama'a da suka bi tawagar.
SHEKARA HUDU AN GAGARA GYARA GADA.
SHEKARA HUDU AN GAGARA GYARA GADA.
.
GA CIKEKKEN RAHOTAN ZIYARAR DA BORNO HAUSA NEWS TA KAI CIKIN GARIN MAIDUGURI.
.
A bayan munyi ziyara a cikin maiduguri babban birnin jihar borno muna cikin tafiya sai muka yi cikibis da wani GADA da ake gyarawa, sai muka sauka muka tambayi mazauna unguwa inda muka ce me sunan wannan unguwa sai suka ce sunan ta Lagos sitirid.
Da muka tambaye su yaushe aka fara wannan GADA da ake yi a unguwar ku? sai suka kada baki suka ce," wannan GADAR yau kusan shekara hudu kenan, har yanzu ba'a gama kammalawa ba, malam baana, yace sun cika unguwar mu da K'URA kuma sun hana al'umma bi ta wannan hanya amma har yau sun gagara gyarawa inji BAANA.
Munci gaba da ziyara a cikin gari ko zamu yi cikibis da wani aiki na azo a gani a cikin maiduguri amma idan mu bai kai gurin ba, har mun bar welcome to na fita zuwa bama amma idan mu bai bamu wani abu sabo ba a cikin maiduguri, hatta manyan titinu na cikin gari idan kana bi zaka iske wasu wurare da suke da ramuka har sai ka dau kan mota a wasu wurare, sai dai wani mai suna BAKURA, magoyi bayan gwamna ne kuma dan jam'iyyar APC yace, "Ai gwamna yana kokari matuka inda ya buga misali da yan gudun hijra yace, ana kula dasu sosai ana basu abunci da ruwan sha da sauran buka tu na yau da kullum dan haka gwamnatin jihar borno tana aiki tukuru, da muka tambaye shi akan cewa, "al'umma suna kokawa wai ba'a gyara musu hanya basu ganin abubuwan more rayuwa ba, sai ya kada baki yace, "ina gwamna ya samu hankalin sa masu fadin haka suyi hakuri anyi kusa gama da yan Boko Haram in an gama dasu zasu ga canji da abubuwa dewa.
.
Sai dai a bangare guda kuma al'umman dake zaune a maiduguri sun musan ta wannan magana inda suka ce, "sam wannan ba dalili ba, gwamna ya labe da batun tsaro yana wawushe kudin jahar su baya musu aiki sannan yan gudun hijra basa samun wata tallafin azo a gani a cikin jihar inda a halin yanzu yan gudun hijra suna gara ramba a cikin gari suna neman abun sawa a bakin salati -inji GARBA DA BAKWOLO.
.
Daga nan sai muka wuce i zuwa san sanin yan gudun hijra wanda yake a kan hanyar da ta fita i zuwa BAMA , a kwai mu dauke da rahoto a nan gaba.
.
GA CIKEKKEN RAHOTAN ZIYARAR DA BORNO HAUSA NEWS TA KAI CIKIN GARIN MAIDUGURI.
.
A bayan munyi ziyara a cikin maiduguri babban birnin jihar borno muna cikin tafiya sai muka yi cikibis da wani GADA da ake gyarawa, sai muka sauka muka tambayi mazauna unguwa inda muka ce me sunan wannan unguwa sai suka ce sunan ta Lagos sitirid.
Da muka tambaye su yaushe aka fara wannan GADA da ake yi a unguwar ku? sai suka kada baki suka ce," wannan GADAR yau kusan shekara hudu kenan, har yanzu ba'a gama kammalawa ba, malam baana, yace sun cika unguwar mu da K'URA kuma sun hana al'umma bi ta wannan hanya amma har yau sun gagara gyarawa inji BAANA.
Munci gaba da ziyara a cikin gari ko zamu yi cikibis da wani aiki na azo a gani a cikin maiduguri amma idan mu bai kai gurin ba, har mun bar welcome to na fita zuwa bama amma idan mu bai bamu wani abu sabo ba a cikin maiduguri, hatta manyan titinu na cikin gari idan kana bi zaka iske wasu wurare da suke da ramuka har sai ka dau kan mota a wasu wurare, sai dai wani mai suna BAKURA, magoyi bayan gwamna ne kuma dan jam'iyyar APC yace, "Ai gwamna yana kokari matuka inda ya buga misali da yan gudun hijra yace, ana kula dasu sosai ana basu abunci da ruwan sha da sauran buka tu na yau da kullum dan haka gwamnatin jihar borno tana aiki tukuru, da muka tambaye shi akan cewa, "al'umma suna kokawa wai ba'a gyara musu hanya basu ganin abubuwan more rayuwa ba, sai ya kada baki yace, "ina gwamna ya samu hankalin sa masu fadin haka suyi hakuri anyi kusa gama da yan Boko Haram in an gama dasu zasu ga canji da abubuwa dewa.
.
Sai dai a bangare guda kuma al'umman dake zaune a maiduguri sun musan ta wannan magana inda suka ce, "sam wannan ba dalili ba, gwamna ya labe da batun tsaro yana wawushe kudin jahar su baya musu aiki sannan yan gudun hijra basa samun wata tallafin azo a gani a cikin jihar inda a halin yanzu yan gudun hijra suna gara ramba a cikin gari suna neman abun sawa a bakin salati -inji GARBA DA BAKWOLO.
.
Daga nan sai muka wuce i zuwa san sanin yan gudun hijra wanda yake a kan hanyar da ta fita i zuwa BAMA , a kwai mu dauke da rahoto a nan gaba.
BUHARI YA NUFI QATAR
A yau Jirgin Shugaba
Muhammadu Buhari Zai Nufi Kasar
Qatar Bayan Kammala Ziyarar Aiki Da
Ibada A Kasar Saudi Arabia.
Shugaba Buhari da shugaban Qatar
da sauran kasashen da ke da man
fetur a duniya, za su tattauna ne kan
matsalar karyewar farashin mai a
kasuwannin duniya
Muhammadu Buhari Zai Nufi Kasar
Qatar Bayan Kammala Ziyarar Aiki Da
Ibada A Kasar Saudi Arabia.
Shugaba Buhari da shugaban Qatar
da sauran kasashen da ke da man
fetur a duniya, za su tattauna ne kan
matsalar karyewar farashin mai a
kasuwannin duniya
AN SOMA YIN SHINKAFA A NIGERIA
Dokokin Buhari Ya Sanya Wasu 'Yan
Kasuwa Soma Raya Masana'antun
Cikin Gida
Kafewar da shugaba Muhammadu
Buhari ya yi na cewa ba zai karya
darajar naira ba ya sanya wasu daga
cikin masu shigo da shinkafa
dawowa gidan don kafa kamfanonin
casar shinkafa a gidan don samar da
shinkafa nagartacciya ga al'ummar
Nijeriya kan farashi mai sauki.
Kwanakin baya ma an sanu wabi
kamfanin shinkafa a jihar Jigawa. A
yau kuma sai ga wata sabuwar
shinkafar gwamnati 'yar jihar Kano.
Wadda gonar "Umza international
farms Ltd" dake kan 13km idan ka
saki hanyar Zaria kafin kwanar
dawaki Kano.
Tuni wasu suka soma nazarin cewa
hakika Buhari ya shirya don samar da
abinci mai sauki ga talaka. Kuma
hakan zai samar da ayyukan yi da
kuma saukin rayuwa a kasa. Wanda
hakan ya sa suke kira ga cewa ya
zama wajibi a baiwa shugaban goyon
baya wajen daina siyan kayan
Kasuwa Soma Raya Masana'antun
Cikin Gida
Kafewar da shugaba Muhammadu
Buhari ya yi na cewa ba zai karya
darajar naira ba ya sanya wasu daga
cikin masu shigo da shinkafa
dawowa gidan don kafa kamfanonin
casar shinkafa a gidan don samar da
shinkafa nagartacciya ga al'ummar
Nijeriya kan farashi mai sauki.
Kwanakin baya ma an sanu wabi
kamfanin shinkafa a jihar Jigawa. A
yau kuma sai ga wata sabuwar
shinkafar gwamnati 'yar jihar Kano.
Wadda gonar "Umza international
farms Ltd" dake kan 13km idan ka
saki hanyar Zaria kafin kwanar
dawaki Kano.
Tuni wasu suka soma nazarin cewa
hakika Buhari ya shirya don samar da
abinci mai sauki ga talaka. Kuma
hakan zai samar da ayyukan yi da
kuma saukin rayuwa a kasa. Wanda
hakan ya sa suke kira ga cewa ya
zama wajibi a baiwa shugaban goyon
baya wajen daina siyan kayan
kasashen waje, muddin ga na gida.
BORNO HAUSA TA SAMU CI GABA
ASSALAMU ALAIKUM WANNAN SHAFI KARI NE DA KUMA CI GABA DA WANNAN KAFA TA BORNO HAUSA NEWS TAKE SAMU DAN HAKA SAI KUCI GABA DA KASAN CE DAMU, KO TA EMAIL A BORNOHAUSA@GMAIL.COM KO TA FACEBOOK MUN GODE .
Subscribe to:
Comments (Atom)